Kwankwaso ko mazabarsa ba zai iya kawo wa ba>> Ganduje
Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Ganduje ya ce tsohon gwamna Rabiu Musa
Kwankwaso ba zai iya lashe zabe a mazabarsa ba, ballantana ya iya kayar
da Shugaba Muhammadu Buhari.
Gwamna Ganduje ya fadi haka ne yayin da aka ruwaito Kwankwason na
ikirarin zai iya kayar da Shugaba Buhari idan PDP ta tsayar da shi
takara.
"Maganar Kwankwaso na nuna cewa ya zama rudadden dan siyasa wanda ke
kama duk wata dama da ta zo masa domin ya dawo da matsayinsa a
siyasance.
"Sama da shekara uku yana Majalisar Dattawa yana barci ba tare da ya
gabatar da kudurin da zai amfani mutanen Najeriya ba," a cewar Ganduje,
wanda tsohon na hannun damar Kwankwaso ne kafin su raba-gari.
bbchausa.
No comments:
Post a Comment